Back

An fara sake zaben Kano cikin lumana a Kura da sauran wurare 

A yau Asabar  aka fara gudanar da zaben ‘yan majalisar dokokin jihar Kano na mazabu shida, tare da isowar kayayyakin zaben da wuri.

An fara zaben da misalin karfe 7:30 na safe inda aka ga jami’an hukumar zabe ta INEC a rumfunan zabe, Kuma aka fara yin rajista da kada kuri’a a lokaci guda da karfe 8 na safe a rumfunan zabe daban-daban.

An samu fitowar jama’a da dama a kananan hukumomin Kura da Garun Malam.

A karamar hukumar Garun Malam kayan zabe sun iso kan lokaci, kuma jama’a sun fito da wuri domin kada kuri’a.

za a sake gudanar da zaben ne a mazabu 60 na mazabu uku na kujerun majalisar dokokin jihar.

Mazabar sun hada da Kura-Garun Malam, Rimin Gado-Tofa, da Kunchi-Tsanyawa.

An gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali a mazabar Rimin Gado da Tofa ba tare da wata tangarda ba.

Jami’an tsaro sun cika a dukkan runfunan zabe, kuma jama’a sun fito gaba daya domin gudanar da aikin da kundin tsarin mulkin kasar ya ba su.

Wakilin Mu
Wakilin Mu
https://www.btvhausa.com

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

× Yaya zan iya taimaka ma ku?