Back

Gwamnan Kano ya sake naɗa Sanusi a matsayin Sarki

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sanar da naɗin Alhaji Muhammadu Sanusi a matsayin sabon Sarkin Kano.

Ya bayyana hakan ne bayan ya rattaba hannu a kan sabuwar dokar da ta kafa masarautar Kano a gidan gwamnati da ke Kano a ranar Alhamis.

Gwamnan ya sanya hannu kan dokar ne da misalin ƙarfe 5:10 na yamma tare da mataimakinsa da Shugaban Majalisar Dokokin Jihar da sauran manyan jami’an gwamnati.

A shekarar 2020 ne tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje ya tsige Sanusi daga karagar mulki, biyo bayan wata rashin jituwa tsakanin su.

Wakilinmu
Wakilinmu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

× Yaya zan iya taimaka ma ku?