Back

Laifukan ta’addanci 141, satar mutane 214, kisan kai 537 aka samu cikin makonni takwas, inji Sufeto Janar na ‘Yan Sanda

Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Nijeriya, Olukayode Egbetokun, a ranar Alhamis, ya ce an kai ƙarar ta’addanci 141, garkuwa da mutane 214 da kuma kisan kai 537 a cikin makonni takwas da suka gabata.

Egbetokun ya ƙara da cewa an kama mutane 3,685 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban, yayin da aka ceto mutane 401 da aka yi garkuwa da su.

Egbetokun ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga ‘yan jarida a Hedikwatar Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Gidan Louis Edet, Abuja.

Ya ce, “Ina farin cikin bayar da rahoton wani gagarumin ci gaba, wanda aka samu ta hanyar aiwatar da dabaru daban-daban da nufin daƙile ƙaruwar miyagun laifuka a faɗin ƙasar nan bayan taron mu na ƙarshe da aka gudanar a ranar 8 ga Fabrairu, 2024.

“A cikin makonni takwas da suka gabata, mun samu ƙararraki 141 na ta’addanci/hare-haren ‘yan aware, da kisan kai 537, da fashi da makami 126, da sace-sacen mutane 214, da kuma laifuka 39 na mallakar bindigogi ba bisa ƙa’ida ba.

“Har ila yau, a tsawon lokacin da Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta kama mutane 3,685 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban, an ceto mutane 401 da aka yi garkuwa da su, an ƙwato bindigogi iri-iri 216, alburusai 3,601 da motoci 82.

“A cikin watanni tara da suka gabata mun ba da kuɗi naira 7,263,391,051.73 ga iyalai 2,5143 na jami’an ‘yan sanda da suka rasu.”

Wakilinmu
Wakilinmu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

× Yaya zan iya taimaka ma ku?